26 Yuli 2026 - 22:05
Source: ABNA24
Hannun Kasar Italiya Dumu-Dumu A Kisan Kiyashin Da Isra’ila Ke Yiwa Falasdinawa

Bayanan hukumar ma'aikatar yaƙi na gwamnatin yahudawa da aka buga kwanan nan, sun nuna cewa 'yan ƙasar Italiya 928 sun shiga cikin kisan kiyashin da Isra’ila k yi a zirin Gaza daga Oktoba 2023 zuwa Maris 2025. Bayyana waɗannan takardun, waɗanda ke nuna haɗin gwiwar Rome da Tel Aviv fiye da dangantakar hukuma, ya haifar da cece-kuce mai yawa a cikin muhawarru na siyasa na Italiya, kuma Stefania Ascari, 'yar majalisar Italiya, ta zargi gwamnatin ƙasarta da gujewa daukar alhakin hakan.

Kamfanin Dillancin Labarai na Ahlul-Bayt (a.s) - ABNA – ya bayar da rahoton cewa: Takardun hukumar ma'aikatar yaƙi na gwamnatin yahudawa da aka buga kwanan nan, sun bayyana cewa 'yan ƙasar Italiya 928 sun shiga cikin ayyukan kisan kiyashin da yahudawa ke yi a zirin Gaza.

Sanarwar ma'aikatar yaƙi ta Isra'ila ta nuna cewa, waɗannan mutane sun shiga cikin kisan kiyashin Gaza daga lokacin Oktoba 2023 zuwa Maris 2025.

A cewar wannan hukuma, sojojin Isra'ila sun je Italiya don hutawa da kuma jinyar tunani bayan halartar yaƙin Gaza, wanda a cewar manazarta, ke nuna ci gaba da wasu matakan haɗin gwiwa tsakanin Rome da Tel Aviv; lamarin da ke sanya matsayin hukumar Italiya game da yaƙi cikin alamar tambaya.

Stefania Ascari, 'yar majalisar Italiya, ta ba da labarin cewa a watan Satumba da ya gabata, ta gabatar da buƙata ga ministocin harkokin waje da na cikin gidan Italiya, don sanar da gwamnati game da kasancewar 'yan ƙasarta a cikin sojojin Isra'ila.

Ascari ta ce: Manufar wannan mataki ita ce, gwamnatin Italiya ta sanar da rawar da 'yan ƙasarta ke takawa a laifukan yaƙi da laifuka a kan bil'adama a Gaza.

Ascari ta shaida wa jaridar "Al-Arabi Al-Jadid" cewa, ta sami amsa daga mataimakin ministan harkokin wajen Italiya, wanda a cikinta ya bayyana cewa ba shi da wani bayani game da waɗannan mutane, kuma Isra'ila ba ta bayyana sunayen sojojin da ke aiki a Gaza ba.

Ascari, tana magana da jami'an Italiya, a martanin da ta mayar ga wannan batu, ta ce: To, ku ce kawai ba ku san komai ba, don ku ƙaurace wa alhakin hakan." Wannan 'yar majalisar Italiya ta bayyana cewa, yarjejeniyar hana da hukunta laifin kisan kiyashi ta Italiya, ba wai kawai tana hukunta masu aikata kisan kiyashi ba, har ma da masu taimaka musu. Ta kuma ce, dole ne gwamnati ta "ɗauki alhakinta" a wannan fanni. "Muna da hakkin sanin yadda ƙasarmu ta shiga cikin kisan kiyashi."

Waɗannan alkaluman, a matakin duniya, suna samun ƙarin mayar da hankali na siyasa da shari'a, domin ƙungiyoyin kare hakkin bil'adama da masana duniya, ciki har da mai ba da rahoto na musamman na Majalisar Ɗinkin Duniya, Francesca Albanese, suna ci gaba da yin gargadi game da manyan ta'addanci, kuma suna buƙatar bincike mai zaman kansa game da aikata laifukan duniya a Gaza.

……………

Alamomi

Ra'ayinka

You are replying to: .
captcha